in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An yanke wa mambobin kungiyar 'yan uwa Musulmi hukunci
2013-09-04 15:01:07 cri
A ranar 3 ga wata, kotun binciken laifuffuka ta soji ta lardin Suez na kasar Masar ta yanke hukuncin daurin rai ga mambobi 52 na kungiyar 'yan uwa Musulmi na kasar, bisa zarginsu da zuga tashe-tashen hankali.

A daya bangare kuma, a ranar 3 ga wata, wata kotun kasar Masar ta yanke hukuncin hana gidan telebijin na Al Jazeera da sauran kafofin telebijin Musulunci 3 watsa shirye-shiryensu a kasar Masar. Haka kuma, kotun ta zargi wadannan kafofin telebijin da kawo baraka ga kasar. Ban da gidan telebijin na Al Jazeera, sauran kafofin sun hada da gidan telebijin da ke karkashin kungiyar 'yan uwa Musulmi ta kasar, da kafofin telebijin na Yarmuk da Al-Quds.

Ministan yada labaru na kasar Masar ya taba bayyana cewa, hana gidan telebijin Al Jazeera gabatar da shirye-shiryensu a Masar zai biya bukatun jama'a, tare da nuna cewa, gidan telebijin din Al Jazeera bai da lasinsin watsa shirye-shiryensu a kasar Masar.(Bako)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China