in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Magoyan bayan Morsy sun yi zanga-zanga a fadin kasar Masar
2013-08-31 18:27:09 cri

Yayin da ake kusa cika watanni biyu da gudanar da zanga-zangar da ta janyo hambarar da shugaba Mohamed Morsy, magoyan bayan Morsy fiye da dubu daya sun yi zanga-zanga a sassa daban daban na kasar Masar a ranar Juma'a 30 ga wata, a wasu wurare masu tarzomar sun fafara da mazauna yankunan da kuma 'yan sanda, lamarin da ya haddasa mutuwar mutane 3, kuma mutane fiye da 10 sun ji rauni.

Bisa kididdigar da hukumar kiwon lafiya ta kasar Masar ta fitar da kuma labarin da kafofin watsa labaru na kasar suka bayar, an ce, a yankin Gabas da jihar Port Said, magoyan bayan Morsy sun yi dauki ba dadi tare da mazaunan jihohin, wanda hakan ya yi sanadiyyar mutuwar mutane 3 baya ga mutane fiye da 10 da suka ji rauni. Kana a jihar Alexandria, da Ad Daqahliyah da sauran jihohin kasar, an samu tashe-tashen hankula a tsakanin magoyan bayan Morsy da masu adawa da su, wadanda ya haddasa raunatar mutane fiye da 10.

Bugu da kari, magoyan bayan Morsy sun yi zanga-zanga a manyan filaye da hanyoyin motoci a birnin Alkahira. Kana darurukan mutane daga cikin masu zanga-zangar sun kewaye wani ofishin 'yan sanda dake Ain Shams, suna masu bukatar da a saki membobin kungiyar 'yan uwa musulmi dake tsare a ofishin. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China