in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Tsohon shugaban kungiyar 'yan uwa Musulmi ya samu bugun ciwon zuciya, in ji wata kafar yada labarai ta Masar
2013-09-01 17:16:32 cri
A ranar Asabar 31 ga wata, tashar yanar gizo ta jaridar Al-Ahram ta gwamnatin kasar Masar ta yi amfani da maganar hukumar tsaro cewa, tsohon shugaban hukumar ba da jagoranci ta kungiyar Muslim Brotherhood, Mohammed Badie, wanda aka tsare shi a yanzu, ya samu bugun ciwon zuciya.

A wannan rana kuma, hukumar harkokin cikin gida ta Masar ta ba da sanarwar musunta labarin mutuwar Mohammed Badie. Tashar yanar gizo ta jaridar Al-Ahram ta rawaito kalaman hukumar tsaro cewa, mahukuntan sun riga sun tura wani rukunin likita zuwa gidan kurkuku na Tora domin ba shi jiyya. Kuma labarin ya kara da cewa, yanzu Mohammed Badie ya riga ya sami sauki.

A karshen watan Yuli, masu kai kara na Masar sun tuhumi Mohammed Badie da wasu sauran manyan jami'an kungiyar Muslim Brotherhood da laifin ta da zaune tsaye, kuma sun bukaci a tsugunar da su a gaban kotun manyan laifuka.

A ran 20 ga watan Agusta, 'yan sandan Masar sun cafke Mohammed Badie mai shekaru 70 a duniya a birnin Nasr dake arewa maso gabashin birnin Alkahira. Daga bisani an tsare shi a gidan kurkuku na Tora dake kudancin birnin Alkahira. Kafin wannan, dansa mai shekaru 38 da haihuwa ya mutu cikin rikicin da aka yi a kusa da filin Ramses na wannan birni.(Fatima)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China