in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Masar ta sanar da kafa rukunin yin gyare-gyare ga tsarin mulki da ke kunshe da mutane 50
2013-09-02 16:38:25 cri
A ranar 1 ga wata, shugaban wucin gadi na kasar Masar Adli Mansour ya ba da umurnin kafa wani kwamitin da ke kunshe da mutane 50, don shirya sabon tsarin mulkin kasar.

Kakakin shugaban kasar ya bayyana cewa, wannan kwamiti zai duba sabon daftarin tsarin mulkin kasar da za a bayar a ranar 8 ga wata. Bisa shirin da Shugaban Mansour ya sanar, an ce, za a kammala aikin dubawa cikin kwanaki 60. Sannan kuma, gwamnatin wucin gadi ta kasar za ta jefa kuri'ar raba gardama game da daftarin cikin kwanaki 30 masu zuwa, idan aka zartas da shi, Masar za ta gudanar da zaben majalisar dokoki cikin kwanaki 15 masu zuwa.(Bako)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China