in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kungiyar EU ta hana mambobinta fitar da makamai ga Masar
2013-08-22 10:53:12 cri
A ranar 21 ga wata, a gun taron ministocin harkokin waje na kasashe mambobin kungiyar EU na musamman da aka yi a birnin Brussels, an yanke shawarar hana mambobin kasashen kungiyar EU da su fitar da makamai ga kasar Masar, don hana tashe-tashen hankali ya ci gaba da tsananta a kasar.

Kafin taron, wasu mambobin kungiyar sun ba da shawara ga kungiyar EU da ta dakatar da shirin samar da kudin agaji da yawansu ya kai kudin Euro biliyan 5 ga kasar Masar da aka amince da shi a watan Nuwanba na bara, amma ganin yanayin tattalin arziki da ake ciki a kasar da damuwa da aka nuna game da zaman rayuwar jama'a a wurin, a karshe dai, ba a sauya wannan shiri a gun taron ba. Sai dai, an bukaci babbar jami'ar kula da harkokin diplomasiyya da tsaro na kungiyar EU Catherine Ashton da kwamitin kungiyar EU da su sake yin nazari game da samar da kudin agaji ga Masar.

Ban da wannan kuma, kungiyar EU ta yi Allah-wadai da tashe-tashen hankali da ya ci gaba da tsananta a kasar Masar, da aika-aikar ta'addanci a kasar. Haka kuma, shirin kungiyar EU ya bukaci bangarorin daban daban na kasar da su dakatar da rikici, da yin hakuri, a sa'i daya kuma, ya bukaci bangarorin siyasa daban daban na kasar da su bi umurnin jama'a, don yin shawarwari ta hanyar siyasa.

A ranar 21 ga wata, a birnin Alkahira hedkwatar kasar Masar, mataimakin sakatare janar na M.D.D. Jeffrey Feldman ya yi shawarwari da ministan harkokin wajen kasar Nabil Fahmy da sakataren janar na kungiyar hadin gwiwa kan kasashen Larabawa AL Nabil el-Araby, don tattauna yanayin tangal-tangal a kasar Masar.(Bako)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China