in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Watakila za a sake jinkirtar da taron Geneva karo na 2 game da batun Syria
2013-08-27 20:55:43 cri
A ranar 27 ga wata a birnin Geneva, Khawla Mattar, kakakin wakilin musamman na MDD da kungiyar kawancen kasashen Larabawa mai kula da batun Syria Lakhdar Brahimi ta bayyana cewa, saboda kasashen Amurka da Rasha sun soka ganawar da aka shirya gudanarwa game da batun Syria a ranar 28 ga wata a birnin Hague, kana ana samun sabon canji kan halin da ake ciki a kasar Syria, watakila za a sake jinkirtar da taron Geneva karo na 2 game da batun Syria.

A makon da ya gabata, Brahimi ya bayyana wa 'yan jarida cewa, bisa shirin da aka tsara, watakila za a gudanar da taron Geneva karo na 2 game da batun Syria a watan Satumba. Wakilan kasashen Amurka da Rasha za su yi shawarwari a birnin Hague a ranar 28 ga watan Agusta, kuma Brahimi da wakilan kasashen biyu za su yi shawarwari a ranar 29 ga wata. Amma a ranar 27 ga wata, kasar Amurka ta sanar da soke ganawar da za a yi a tsakaninta da kasar Rasha.

Madam Mattar ta tabbatar a gun taron manema labaru da aka gudanar a birnin Geneva a wannan rana cewa, kasar Amurka ce ta gabatar da kudurin soke ganawar a birnin Hague.

Kana Mattar ta jaddada cewa, a ganin Brahimi, tsanantar halin rikici a kasar Syria ya bayyana cewa, amfani da karfin tuwo zai kara kawo illa ga fararen hula a kasar, kuma hanyar siyasa ita ce hanya daya kawai ce wajen warware batun. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China