in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasashen duniya suna fatan kasar Sin za ta kara ba da gudummawa wajen raya tattalin arzikin G20 da na duniya baki daya
2013-08-29 16:24:21 cri
A ranar 5 da 6 ga watan Satumba, za a yi taron koli karo na 8 na shugabannin kasashen G20 a birnin Saint-Petersbourg dake kasar Rasha. Shugaban kasar Sin Xi Jinping zai halarci taron. Kwanan baya, kwararru da masana na wasu kasashe sun bayyana cewa, kasar Sin ta tashi tsaye don shiga cikin hadin gwiwa da ke tsakanin kasashen duniya a karkashin inuwar G20, kuma suna fatan kasar Sin za ta kara ba da gudummawa wajen raya tattalin arzikin duniya.

Shehun malami a kwalejin koyon hada-hadar kudi na Frankfurt da ke kasar Jamus Horst Löchel ya bayyana cewa, a matsayin wata babbar kasa wadda ta samu bunkasuwa cikin hanzari, kuma wakilin kasashe masu saurin bunkasuwa, kasar Sin za ta ci gaba da taka muhimmiyar rawa a yayin taron koli na G20. Tattalin arzikin kasar Sin ya samu bunkasuwa lami lafiya, kuma zai ci gaba da taka muhimmiyar rawa wajen yaki da rikicin kudi na duniya, da sa kaimi ga farfado da tattalin arziki.

Shehun malami a sashen tattalin arziki na jami'ar Mexico Alejandro Martínez ya bayyana cewa, a matsayin gamayyar tattalin arziki mafi girma ta biyu a duniya, kasar Sin ta dauki matakan hadin gwiwa yadda ya kamata a karkashin inuwar kungiyar kasashen G20. Yana fatan kasar Sin za ta ci gaba da taka muhimmiyar rawa wajen daidaita dangantakar da ke tsakanin kasashe masu wadata da kasashe masu tasowa, don sa kaimi ga samun daidaito a tsakaninsu.(Bako)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China