in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin ta bukaci Ghana da ta kiyaye tsaro da hakkin Sinawa a kasar
2013-06-13 20:18:06 cri
A ranar Alhamis 13 ga wata, a nan birnin Beijing, mai magana da yawun ma'aikatar harkokin waje ta Sin Hua Chunying ta yi bayani cewa, Sin ta tura wani rukunin aiki da ma'aikatar harkokin waje da ta cinikayya da kuma hukumar 'yan sanda ta Sin suka kafa, zuwa kasar Ghana, domin share fagen batun kiyaye tsoro da hakkin Sinawa masu hakar ma'adinin zinari yadda ya kamata.

Hua Chunying ta ce, Sin ta bukaci Ghana da ta gudanar da bincike bisa dokoki yadda ya kamata, da dakatar da kame Sinawa a waje da yankunan hakar ma'adinai, da dakatar da ayyukan harin da wasu mutanen wurin suke kai wa Sinawan tare da kwace masu dukiyoyi, da kuma tabbatar da tsaron Sinawa da suke son komawa gida Sin, da kiyaye kayayyakin ayyukan su da sauran dukiyoyin su bisa iyakacin kokari.

Yanzu dai an riga an saki duk Sinawa 169 da aka cafke a Ghana.(Fatima)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China