in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Bankin kasar Sin ya maido da bayar da kudin ayyukan iskar gas a Ghana
2013-07-13 15:48:10 cri
Kamfanin iskar gas na kasar Ghana (GNGCL) ya bayyana wa kamfanin dillancin labaran kasar Sin, Xinhua ranar Jumma'a cewa bankin bunkasa na kasar Sin (CDB) ya maido da sakin kudin rance ga kamfanin SINOPEC domin ayyukan bunkasa masana'antar iskar gas a yammacin kasar Ghana.

Kudaden da aka bayar a ranar Laraba ya kawo adadin kudade da aka sake zuwa dalar Amurka miliyan 446.93.

Da yake amsa tambayoyi daga Xinhua, darektan harkokin sadarwa na kamfanin iskar gas na kasar Ghana Guure Brown,Guure ya baiyana cewa ana biyan 'yan kwangila da kuma kamfanin SINOPEC ne bayan an karbi kudi daga rancen da bankin CDB ya bayar.

Kamfanin man fetur na kasar Sin (SINOPEC Group) wani babban kamfani ne na albarkatun man fetur da aka kafa a shekarar 1998 a madadin tsohon hukumar man fetur ta kasar Sin. (Lami Ali)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China