in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ana gudanar da ayyuka yadda ya kamata a garin Changdu na jihar Tibet, sakamakon bala'in girgizar kasa
2013-08-14 15:00:35 cri
Ya zuwa karfe 12 na ranar 13 ga wata, girgizar kasa da ta auku a yankin Changdu na jihar Tibet ta kasar Sin ta yi illa ga gundumomi 11, garuruwa 114 da kuma mutane dubu 570, inda har gidaje sama da dubu 45 suka lalace.

A halin yanzu dai, ana gudanar da ayyukan yaki da bala'in girgizar kasa yadda ya kamata, kuma bisa rahoton da aka samu, babu wanda ya rasu ko kuma ya bace sakamakon bala'in a yankunan.

Shugaban hukumar kula da harkokin girgizar kasa ta jihar Tibet ya bayyana cewa, girgizar kasa da ta auku a wannan karo a yankin Changdu girgizar kasa ce mafi muni tun bayan shekaru 10 da suka gabata.

Hukumar kula da harkokin jama'ar jihar Tibet ta bayyana cewa, ya zuwa yanzu an riga an aika da kayayyakin agaji da suka hada da tantuna guda 1200, abinci ton 30, manyan barguna na zamani guda dubu 20, ruwan sha kwalba dubu 4, da kuma abincin dabbobi ton 110 zuwa yankunan da bala'in ya shafa. Bugu da kari, wasu kungiyoyin ba da agaji da kuma na ba da jinya sun riga sun isa yankunan don gudanar da ayyukansu yadda ya kamata. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China