in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban kasar Sin ya bukaci a kara kokarin gudanar da aikin ceto da yaki da bala'in girgizar kasa
2013-07-22 20:21:59 cri

A safiyar ranar Litinin 22 ga wata da misalin karfe 7 da minti 45, aka samu abkuwar girgizar kasa mai karfin maki 6.6 a gundumar Min da ta Zhang ta birnin Dingxi na lardin Gansu. Ya zuwa karfe 5 na yammacin wannan rana, gaba daya mutane 75 ne suka mutu yayin da wasu sama da 600 suka jikkata a sakamakon haka.

Shugaban kasar Sin Xi Jinping ya mai da hankali sosai kan wannan batu, inda ya bukaci lardin Gansu da hukumomin da abin ya shafa da su kara kokarin yaki da bala'in girgizar kasa, tare da gudanar da aikin ceto yadda ya kamata, a kokarin rage yawan mutanen da za su mutu a sakamakon hakan.

Mr Xi Kuma ya bukaci a kara kulawa da mutane domin tsira daga bala'in da kuma tsugunar da su, da kara sa ido kan tartsatsin girgizar kasa, a kokarin daukar matakan yaki da sake abkuwar bala'in, da zummar rage hasarar da aka samu.

Firaministan Sin Li Keqiang shi ma ya bukaci hukumomin da abin ya shafa da su dauki matakai nan take, tare da tura rukunonin aiki da kwararru zuwa yankuna da bala'in ya abkawa, a kokarin ba da jagoranci kan yaki da bala'in da gudanar da aikin ceto.(Fatima)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China