in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Bincike ya nuna cewa, bangarorin dake gaba da juna a Siriya dukansu sun yi amfani da makamai masu guba
2013-06-05 16:50:45 cri
A ranar 4 ga wata, hukumar bincike ta kasa da kasa mai zaman kanta game da batun Siriya ta M.D.D. ta mika wani rahoto ga wurin taron kwamitin kare hakkin dan Adam na M.D.D. karo na 23 da ake yi a birnin Geneva, inda rahoton ya tabbatar da cewa, gwamnatin Siriya da dakarun adawa da gwamnatin dukansu sun yi amfani da makamai masu guba cikin rikicin da aka yi tsakaninsu.

Kuma rahoton ya yi bincike da kuma tantancewa game da batun kare hakkin dan Adam a kasar Siriya daga ranar 15 ga watan Janairu zuwa ranar 15 ga watan Mayu. A cikin rahoton, an ce, gwamnatin Siriya na mallakar makamai masu guba, kuma dakaru masu adawa da gwamnatin su ma, kila sun samu kuma sun yi amfani da makamai masu guba. Sabo da haka, masana sun yi imanin cewa, daga watan Maris zuwa Watan Afrilu, an yi amfani da makamai masu guba cikin rikicin Siriya, amma sai a samu cikakkiyar shaida daga wurin rikicin kawai, za a iya yanke magana a karshe.(Bako)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China