in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Amurka ta rufe ofisoshin jakadancinta guda 22 da ke kasashen waje sakamakon harin da kila kungiyar Al-Qaida za ta yi
2013-08-03 18:23:51 cri
Ranar 2 ga wata, kasar Amurka ta yi gargadi ga 'yan kasarta dangane da yin tafiye-tafiye a duk fadin duniya, inda ta yi kashedin cewa, kila kungiyar Al-Qaida da ressanta za su kai harin ta'addanci a yankunan Gabas ta Tsakiya da arewacin Afirka, don haka ya zama tilas mutanen Amurka da ke yankunan su yi taka tsan-tsan. Sabili da haka ne ma majalisar harkokin wajen Amurka ta sanar da cewa, a ranar 4 ga wata, za a rufe ofishoshin jakadanci na Amurka guda 22 da ke kasashen waje, ciki had da kasashen Yemen, Masar, Saudiya, Jordan, Iraki, Afghanistan, da Libya.

Gidan talabijin din CNN ya ambato jami'an Amurka da suke da masaniya kan lamarin da cewa, sakamakon gabatowar karshen Ramadan, 'yan kungiyar Al-Qaida da ke Yemen suna gaggauta kulla makarkashiyar kai hari kan mutanen Amurka da na kasashen yammacin duniya, musamman ma wadanda suke kaiwa da kawowa a Gabas ta Tsakiya da arewacin Afirka. Daga ranakun 3 zuwa 6 ga watan da muka ciki, ofishin jakadancin Amurka da ke kasar ta Yemen ya fi fuskantar hadari, musamman ma a ranar 4 ga wata, inda kila a wannan rana ce 'yan ta'adda za su kai hari.

Jami'an sun kara da cewa, in halin da ake ciki bai canza ba bayan ranar 4 ga wata, to, kila za a ci gaba da rufe wasu ofisoshin jakadancin Amurka da ke kasashen waje. (Tasallah)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China