A cikin wannan rana da safe, wajen karfe 6, 'yan kunar bakin waken sun tuka motoci biyu da aka dasa bama bamai cikin sansanin cikin sauri, daga baya, an samu musayar wuta tsakanin bangarori biyu ta kusan awoyi biyu. Kungiyar Taliban ta dauki alhakin wannan hari, wanda ya kasance hari mafi girma a cikin hare-haren da suka faru a sansanin sojojin saman da ke birnin Jalalabad tun watan Fabrairu na shekatar bana.
Hukumar 'yan sanda kasar Afghanistan ta bayyana cewa, dakaru 9 ne suka kai wannan hari, 3 daga cikinsu sun mutu sakamakon fashewar bam, a yayin 6 suka mutu a cikin musayar wuta. Bangaren NATO ya dauka cewa, masu kai harin ba su cimma burinsu ba saboda ba wanda da ya kai harin ya shiga babbar kofar sansanin. (Maryam)