Mr. Mamnoon Hussain ya cimma nasara ne a zaben da kuri'u 432, yayin da abokin hamayyarsa Wajihuddin Ahmed na jam'iyyar Tehreek-e-Insaf ya samu kuri'u guda 77.
Shugaban kasar na yanzu Asif Ali Zardari zai kammala wa'adin aikinsa ran 8 ga watan Satumba shekarar bana, don haka nan da wata daya za a rantsar da Mr. Mamnoon Hussain a matsayin shugaban kasar. (Maryam)