in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Fadar shugaban kasar Masar ta ce ba tada niyyar aza dokar ta bace cikin gaggawa
2013-07-30 11:03:51 cri
Mai bada shawara kan harkokin watsa labarai na fadar shugaban kasar Masar, Ahmed al-Mislimani, ya furta cewa kasarsa ba zata aza dokar ta bace ba a halin yanzu, a wani labari da gidan talabijin na kasar ya rawaito. A yayin wani taron manema labarai, mista Mislimani ya nuna cewa, baiwa firaminstan kasar wasu sassan iko da shugaban kasa yayi, ba ya nufin wannan doka za'a awaitar da ita cikin gaggawa.

A ranar Lahadi, bisa wani yunkuri, shugaban mulkin wucin gadi Adli Mansour ya gabatar da wani kuduri, wanda janyo jita jitar mutane dake bayyana cewa wannan kuduri zai kasance wani mafarin farautar 'yan gani kashenin shugaba Mohamed Morsi, da suka fara kai hare hare kan jami'an tsaro a yankin Sinai.

Amma kuma mista Mislimani ya bayyana cewa wannan mataki na shugaba Adli Mansour an dauke shi ne bisa manufar cimma ikon kasa. Duk da kawar da zancen dake nuna cewa wannan doka zata fara aiki cikin gaggawa, mashawarcin shugaban kasa ya jaddada cewa wasu abubuwan tashe tashen hankali da suka faru na baya baya na bukatar ganin an kafa wannan mataki domin kiyaye zaman lafiyar kasa. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China