in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ban Ki-Moon ya yi kira ga bangarori daban daban na Masar da su yi hakuri
2013-07-26 16:29:43 cri
Ran 25 ga wata, ta bakin kakakinsa, babban sakataren MDD Ban Ki-Moon ya ba da wata sanarwa, inda ya yi kira ga bangarori daban daban na kasar Masar da su yi hakuri daidai iyakacin hakuri, kuma ya sa musu kaimi don su yi shawarwari daga duk fannoni ciki har da yin yunkurin neman sulhu tsakaninsu.

Cikin sanarwar, Ban Ki-Moon ya nuna goyon baya ga ikon jama'ar kasar Masar wajen yin zanga-zanga cikin lumana, ya kuma yi kira ga gwamnatin wucin gadi ta kasar da ta tabbatar da dokokin shari'a da oda, sa'an nan kuma ta kiyaye tsaron al'umman kasar, a kuma daina kama mutane ba tare da wata hujja ba, kana ya kamata gwamnatin ta saki shugaba Mohamed Morsy wanda aka hambarar daga mukaminsa da ma sauran shugabannin kingiyar 'yan'uwa Musulmi ba tare da bata lokaci ba, sa'annan ta gudanar da cikakken bincike kan lamarin.

Bayan rundunar sojan kasar Masar ta hambarar da Mohamed Morsy daga mukaminsa ran 3 ga watan nan da muke ciki, ana ci gaba da samun rikice-rikice tsakanin jam'iyyu daban daban na kasar.

Sakamakon haka, a ran 25 ga wata, rundunar sojan kasar ta yi gargadi ga jam'iyyar 'yan'uwa Musulmi da ta shiga shawarwari na duk kasa baki daya cikin awoyi 48, in ba haka ba, rundunar sojan kasar za ta dauki matakai don yaki da aikace-aikacen tashin hankali da na 'yan ta'adda a kasar. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China