in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Babban magatakardar MDD ya yi tir da barkewar tashin hankali a Masar
2013-07-29 10:35:00 cri
Babban magatakardar MDD Ban Ki-Moon ya nuna matukar damuwarsa ga barkewar tashin hankalin da ya yi sanadiyar rasuwar mutane sama da 70, tare da jikkata wasu da dama a wasu sassan kasar Masar, yayin da magoya bayan hambararren shugaban kasar Mohammed Morsi suka yi arangama da dakarun sojin kasar a karshen makon da ya gabata.

Yayin wata tattaunawa da ya yi ta wayar tarho ranar Lahadi 28 ga wata, da mataimakin shugaban kasar ta Masar Mohamed El-Baradei, Mr. Ban ya bayyana rashin gamsuwarsa da yadda al'amura ke wakana a kasar, yana mai bayyana matukar bukatar da ake da ita ga mahukuntan kasar na daukar matakan da suka dace, don warware matsalolin siyasar kasar ta hanyar lumana.

Daga nan sai ya nanata bukatar sakin tsohon shugaban kasar Mohammed Morsi, wanda mahukuntan kasar kewa daurin talala, tare da ragowar magoya bayan kungiyar 'yan uwa musulmi da aka kame, ko kuma a tabbatar da gudanar da bincike kan su bisa tsari na adalci.

A wani ci gaban kuma shugaban kasar ta Masar na rikon kwarya Adli Mansour, ya bayyana amincewarsa da baiwa Firaministan kasar Hazem Beblawi wani yanki na ikonsa, don gane da batun daukar matakan dake kunshe cikin dokar ta baci, matakin da ake ganin zai iya baiwa Beblawi damar umartar sojoji su damke, tare da tsare fararen hula, musamman wadanda ake gani na zamewa gwamnatin rikon kwaryar kasar kadangaren bakin tulu. (Bello Wang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China