in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Angola ta tura masu sa ido ga gudanar zabe zuwa Zimbabwe.
2013-07-24 10:05:46 cri
Wata tawaga mai kunshe da manyan jami'an gwamnatin kasar Angola su 28 ta sauka a Zimbabwe, domin gudanar da aikin sa ido ga yadda babban zaben kasar zai gudana.

Wata sanarwa daga ma'aikatar harkokin wajen Angola ta bayyana cewa tawagar ta sauka kasar Zimbabwe ne tun ranar Alhamis 18 ga wata, karkashin jagorancin Sandro de Oliveira, daraktan ofishin kungiyar SADC dake karkashin ma'aikatar wajen Angola, za kuma ta nazarci yadda zaben da ake fatan kadawa ran 31 ga wata zai wakana.

Jimillar jami'an dake kunshe cikin tawagar jami'an da zasu yi aikin sa ido ga zaben dake tafe, karkashin kungiyar habaka ci gaban kasashen Kudancin Afirka ta SADC dai yanzu haka sun kai 235, ana kuma sa ran wannan adadi ya kai mutum 300 nan da lokacin fara gudanar da zaben. (Saminu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China