in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban wucin gadi na Masar ya nada mataimakin shugaba da firaminista na wucin gadi
2013-07-10 11:05:36 cri
Bisa labarin da aka samu a ran 9 ga wata, an ce, a wannan rana, shugaban wucin gadi na kasar Masar Adli Mansour ya nada Mohamed El-Baradei, daya daga cikin shugabannin kungiyar kawancen jam'iyyun adawar kasar, a matsayin mataimakin shugaban wucin gadi, yayin da tsohon firaminista, kuma ministan harkokin kudin kasar, Hazem el-Beblawi ya zamo sabon firaministan wucin gadin kasar.

Rahotanni sun nuna cewa, shugaba Mansour ya nada shugaban gungun kawancen jam'iyyun adawar kasar ko "kungiyar fafitikar 'yantar da al'umma " kuma tsohon babban darektan hukumar makamashin nukiliya ta duniya, Mohamed El-Baradei a matsayin mataimakin shugaban gwamnatin wucin gadin kasar ne, don ya kula da harkokin kasashen waje, a hannu guda kuma, aka nada Hazem el-Beblawi a matsayin firaministan wucin gadi, don ya kafa gwamnatin wucin gadin kasar. Tuni dai Beblawi ya kama aikin zaben jami'an gwamnatin wucin gadi.

Jim kadan da sanar da nadin jami'an biyu, ministan kula da harkokin tsaron kasar Abdel Fattah al-Sisi, ya ba da jawabi ta gidan talabijin na kasar ta Masar, inda ya yi gargadi da a kauracewa dukkan abubuwan daka iya kawowa yunkurin kafuwar gwamnatin wucin gadin kasar illa. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China