in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Masu zanga-zanga da dama sun mutu ko jikkata a kasar Masar
2013-07-06 16:24:17 cri

Bayan abkuwar rikicin siyasa a kasar Masar, an samu barkewar hargitsi da zubar da jini a wurare da dama a kasar. A ranar 5 ga wata, masu goyon bayan Mohamed Morsy fiye da dubu 10 sun yi zanga-zanga a titunan dake biranen Alkahira, Alexandria da sauran wurare, inda suka ta da tarzoma da masu adawa da Mohamed Morsy da sojoji da kuma 'yan sanda, lamarin da ya yi sanadiyyar mutuwar mutane a kalla 24, yayin da wasu fiye da dubu 1 suka jikkata.

A wannan rana, hargitsin da ya abku a Alexandria ya yi sanadin mutuwar mutane 12, yayin da wasu 5 suka rasa rayuka a cikin hargitsin da aka samu a dab da fadar shugaban kasar da ke birnin Alkahira da filin Tahrir. Sa'an nan kuma mutane 5 sun mutu sakamakon hargitsin da aka samu a tsibirin Sinai, yayin da wani ya mutu cikin hargitsin da ya barke a lardin Suez, wani kuma ya mutu cikin hargitsin da ya abku a lardin Asyut.

A ranar 5 ga wata, ta bakin kakakinsa, Ban Ki-moon, magatakardan MDD. ya ba da wata sanarwa, inda ya yi kira ga rundunar tsaron kasar ta Masar da ta hana barkewar hargitsi, da tabbatar da tsaron lafiyar masu zanga-zanga, ya kuma yi kira ga jama'ar Masar da su yi amfani da hakkokinsu cikin ruwan sanyi.

Sanarwar ta ce, kamata ya yi dukkan jama'ar kasar ta Masar su tsai da kuduri kan makomar kasarsu bisa ka'idar girmama banbance-banbance na ra'ayin siyasa, kana a danka wa shugabannin kasar nauyin shirya wata tattaunawar dimokuradiyya cikin lumana, inda kowa da kowa zai iya halarta.(Tasallah)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China