in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Jihar Borno ta Nijeriya tana fatan inganta hadin gwiwa da kasar Sin wajen aikin gona
2013-07-05 13:35:56 cri
A ranar 4 ga wata, a wata hirar da Gwamnan jihar Borno Alhaji Kashim Shettima ya yi da wakilinmu, ya bayyana cewa, jiharsa na fatan inganta hadin gwiwa da kasar Sin a wajen aikin gona, don taimakawa wajen kawar da talauci da samar da abinci wanda ta haka ne, za a cimma burin samar da isasshen abinci ga 'yan jihar da canja salon aikin gona.

Alh. Shettima ya ce, a lokacin da ziyara a nan kasar Sin, ya ce, aikin gona na zamani na kasar Sin ya burge shi sosai, kuma a ganinsa, dalilin da ya sa aikin gona na Sin ya cimma nasara shi ne sabo da injunan zamani da irin hatsi mai kyau, da kuma takin zamani mai inganci da kasar Sin take da shi. A cikin shekaru goma-gomai, Sin ta warware matsalar samar da abinci ga al'ummar kasar da yawansu ya kai biliyan 1 da wani abu, kana ta kawar da talauci da yunwa da aka yi fama da su, sabo da haka, jihar Borno tana fatan koyon fasahohi daga kasar Sin, don ci gaba da inganta hadin gwiwa wajen aikin gona da kasar Sin, ta haka, za a iya warware matsalar noman rani da ke ci wa jihar tuwo da kwarya.

Ban da wannan kuma, Gwamnan ya bayyana cewa, yana fatan inganta hadin gwiwa da kamfanonin samar da na'urori masu amfani da hasken rana don samar da wutan lantarki na kasar Sin, don samun damar warware matsalar wuta a kuma raya aikin gona na zamani a jihar.(Bako)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China