in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
'Yan wasan kwallon kwando na Nijeriya suna fatan inganta dankon zumunci tsakanin kasashen Sin da Nijeriya
2013-07-04 16:25:16 cri
Bayan da aka kammala gasar wasan kwallon kwando ta Stankovic ta shekarar 2013, a lardin Lanzhou da ke kasar Sin a hukunce, a ranar 5 ga wata, za a bude wannan gasa a birnin Guangzhou, kuma a yayin gasar, kungiyar wasan kwallon kwando ta Nijeriya za ta kara takwaranta da na kasar Sin, don gane da hakan, 'yan wasan na Nijeriya sun bayyana cewa, suna fatan yin amfani da gasar don yaukaka dankon zumunci da ke tsakanin kasashen biyu.

Yayin da daya daga cikin 'yan wasan kasar Nijeriya Abubakar Usman ke zantawa da wakilinmu, ya bayyana cewa, duk da cewa, a zangon Lanzhou, kungiyar wasan kwallon kwando ta Nijeriya ta lashe kungiyar ta Sin, amma ya ce, irin sakamakon gasar ba ya da muhimmanci sosai, abin da ya fi muhimmanci shi ne, a yi amfani da gasar don kara dankon zumunci da ke tsakanin kasashen Nijeriya da Sin, da kara kwarewar wajen wasanni.

Ban da wannan kuma, Abubakar ya jinjinawa kokarin da kasar Sin ta yi wajen karbar bakunci gasar. Ya ce, zangon Lanzhou da na Guangzhou, masu shirya gasar sun yi aiki ainun, abun da ya sa 'yan wasan jin dadin zama tamkar a gida. Ya kuma nuna godiya ga masu shirya gasar, yana fatan tattalin arzikin kasar Sin zai ci gaba da habaka, kuma zaman rayuwar jama'a zai kara samun kyautatuwa.(Bako)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China