in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugabannin kasashen Afrika 25 za su fara wani babban taro a Yaounde na Kamaru
2013-06-24 15:23:46 cri

Shugabanni bakwai na kungiyar tattalin arzikin kasashen dake tsakiyar Afrika (CEEAC) da na kungiyar tattalin arzikin kasashen yammacin Afrika ECOWAS sun isa birnin Yaounde na kasar Kamaru tun ranar Lahadi domin halarta babban taro na kwanaki biyu kan batutuwan kiyaye tsaro a yankin tekun Guinee da za'a bude ranar Litinin a karkashin jagorancin MDD. Shugabannin kasashe kamar su Mahamadou Issoufou na Nijar, Goodluck Ebele Jonathan na Nijeriya, Manuel Pinto da Costa na Sao Tome-Principe, Teordoro Obiang Nguema Mbasogo na Guinee-Equatoriale, Thomas Boni Yayi na kasar Benin, Blaise Compaore na Burkina-Faso da kuma Denis Sassou Nguesso na kasar Congo-Brazaville sun isa babban birnin kasar Kamaru domin wannan taro, tare kuma da mataimakiyar shugaban kasar Gambia, madam Isatou Njie Saidou. A cewar wata majiya mai tushe daga hukumomin kasar Kamaru, sauran shugabanni kamar su Ali Bongo Ondimba na kasar Gabon, Idriss Deby Itno na kasar Chadi da Alassane Ouatttara na kasar Cote d'Ivoire za su isa ranar Litinin da safe a kasar ta Kamaru. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China