in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kogin Nile na da isasshen ruwa domin biyan bukatun kasashen dake bakinsa
2013-06-21 15:06:17 cri
A ranar 20 ga wata, bisa labarin da kamfanin dillancin labaru na MENA na kasar Masar ya bayar, an ce, karamin ministan harkokin wajen kasar Habasha Berhane Gebre-Christos ya bayyana cewa, Habasha ta san irin hali ne dogara bisa kogin Nile daga kasar Masar, amma, idan aka bi ka'idar girmama moriyar juna don raya kogin Nile, za a gano cewa, kogin Nile na da isasshen ruwa da zai biya bukatun kasa da kasa dake bakinsa.

Bisa labarin da aka bayar, an ce, Berhane Gebre-Christos ya yi imani cewa, kogin nil zai zama tamkar wata gada don inganta hadin gwiwa tsakanin kasashen Habasha da Masar, amma a sa'i daya kuma, ya bayyana cewa, yana fatan Masar za ta girmama hakkin raya albarkatun da Allah ya fuwace wa kasar Habasha.

Domin gina wata madatsar ruwa mai suna Renaissance da za ta samar da wuta megawatt dubu 6, kwanan baya, kasar Habasha ta fara yin gyare-gyare game da sassan hanyoyin kogin Nil, abin da ya kawo damuwa daga kasar Masar game da albarkatun ruwa na kasar. Game da matakin da kasar Habasha ta dauka, shugaban kasar Masar Mohamed Morsi ya bayyana cewa, 'Idan akwai bukata, za mu yi amfani da jininmu don kiyaye kogin Nil.''

Bisa yarjejeniyar da aka daddale a tsakiyar karnin 20, an ce, kasar Masar da makwabtarta Sudan suna da hakkin yin amfani da kogin Nil, amma sauran kasashen da kogin Nil ya malala ya bi su sun bayyana cewa, wannan yarjejeniya ba ta dace da bukatun samun bunkasuwa na zamani ba. (Bako)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China