in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban kasar Masar ya sanar da cewa, zai canja membobin majalisar ministocin kasar
2013-04-21 17:01:30 cri
Shugaban kasar Masar Mohamed Morsy ya sanar a shafinsa na Twitter a ranar 20 ga wata cewa, zai canja membobin majalisar ministocin kasar wandanda ke karkashin jagorancin firaministan kasar Hisham Qandil a halin yanzu.

Shugaba Morsy ya ce, za a canja membobin majalisar ministocin kasar ne don ci gaba da yin kokarin cimma burin da aka tsara a shekarar 2011 lokacin da aka yi zanga-zanga mai tarin yawa a kasar, tare da tabbatar da shigar da fitattun mutane a majalisar ministocin kasar. Kana ya ce, za a canja wasu gwamnonin jihohin kasar.

Shafin internet na Pyramids Online ya tabbatar da wannan labari, amma ya ce, shugaba Morsy bai sanar da ko za a canja firaministan kasar Qandil ba ko kuma a'a.

Bisa labarin da aka bayar, an ce, shugaba Morsy ya bayyana cewa, za a canja membobin majalisar ministocin kasar bisa bukatun jama'a, ministocin da jama'ar kasar da dama suke goyon baya za su ci gaba da zama mukaminsu, yayin da za a canja wadanda jama'ar kasar ke nunawa rashin goyon baya. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China