in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Bankin duniya ya sa niyyar rubanya tallafinsa zuwa kasar Nijar
2013-06-07 10:39:17 cri

Bankin duniya ya dauki niyyar rubanya taimakonsa ga kasar Nijar ta hanyar zuba jari a wannan kasa, daga dalar Amurka miliyan 400 zuwa fiye da dalar Amurka miliyan 800, in ji darektan ayyukan bankin duniya mista Ousmane Diagana bayan wata ganawarsa tare da shugaban kasar Nijar Mahamadou Issoufou.

Bankin duniya na gudanar da ayyuka da dama a kasar Nijar kuma wannan taimako zai shafi fannonin ilmi, kiwon lafiya, jama'a, noma, kiwo, cigaban yankuna da na karkara da ma'aikatun kudi na gwamnati, in ji mista Diagana.

Haka kuma jami'in ya gabatar da ta'aziyar bankin duniya bayan hare-haren ta'addanci na biranen Agadez da Arlit da kuma gidan kurkukun birnin Yamai.

An yi gasanar a gaban ministan harkar kasa, dake kula da fasalin kasa Amadou Boubacar Cisse da kuma wakilin bankin duniya dake kasar Nijar Ernest Koffi. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China