in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kwadibwa ta tura masu sa ido kan barkewar rikici a fadin kasar
2013-06-07 10:23:17 cri

Hukumar yaki da bazuwar kananan makamai a kasar Kwadibwa (COMNAT-ALPC), ta bayyana ranar Laraba cewar, an tura jami'an cibiyar sa ido kan alamun barkewar rikici, (OVA) a fadin kasar baki daya.

A cikin watan Disambar bara, hukumar ta kafa wannan cibiyar dauke da manufar cimma shirye-shiryenta.

A cikin wata sanarwa, hukumar COMNAT-ALPC ta bayyana cewa, bayan da aka kammala gwajin wannan shiri, ana kokarin fadada aikin zuwa al'umomi da garuruwa guda 107.

An yi wa jami'an horaswa kan yadda za su taro bayanai, su rubuta, su kuma tsara su ta wani fasali, da kuma aikawa da bayanin domin a samu tabbatar da bayani ko kuma yanayi da aka samu barkewar rikici.

Mataimakin babban sakataren hukumar Anzian Kouadja ya ce, za'a shirya wasu tarukan samar da horo, a cikin watanni uku masu zuwa, domin cibiyar ta samu isa fadin kasar baki daya, ta kuma taimakawa gwamnati a kan yaki da safara da kuma bazuwar kananan makamai ba bisa ka'ida ba, a kasar baki daya. (Lami)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China