in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ana yakin fadakarwa a Cote d'Ivoire domin bunkasa aikin noma
2013-05-13 11:19:16 cri

Ministan noman kasar Cote d'Ivoire zai fara wani rangadi tun daga ranar Laraba mai zuwa na yakin wayar da kan jama'a da fadakarwa domin sake bunkasa aikin samun albarkatun noma a yankunan tsakiya, arewacin kasar da arewa maso gabas da rikicin siyasa ke ratsawa daga shekarar 2002, tare kuma da barkewar tawaye har zuwa shekarar 2010 a cikin rabin arewacin kasar Cote d'Ivoire.

Wannan shela tana cikin tsarin aiwatar da wani shirin tallafawa samun albarkatun noma da kasuwancinsu da aka kaddamar a ranar 15 ga watan Disamban shekarar 2012 a Bouake, ta hanyar mai da hankali ga noman gandari na shimkafa, masara da kayan lambu.

Ana ganin wannan aiki zai taimaka wajen sake bunkasa samun albarkatun noma, musammun ma a bangaren cimaka a cikin jihohi 12 na wannan yanki da abun ya shafa bisa burin taimakawa rage talauci a yankunan karkara, ta yadda za'a taimakawa cigaban tattalin arziki a wadannan yankuna da aka kebe. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China