in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasashe 6 da batun nukiliya na Iran ya shafa sun bukaci Iran da ta dakatar da aikace-aikacen nukiliya
2013-06-06 16:46:14 cri
A ranar 5 ga wata, a gun taron kwamitin hukumar kula da makamashin nukiliya ta duniya wato IAEA da aka yi a birnin Vienna, kasashe 6 da batun nukiliya na kasar Iran ya shafa wato Amurka, Birtaniya, Faransa, Rasha, Sin da Jamus, sun ba da sanarwa cikin hadin gwiwa, inda suka bukaci Iran da ta dakatar da aikace-aikacen tace nukiliya da suka keta kudurin kwamitin sulhu na M.D.D..

A cikin sanarwar, an dora muhimmanci sosai game da shirin nukiliya na kasar Iran, da bukatar Iran da hukumar IAEA da suka yi hadin gwiwa daga dukkan fannoni, da gaggauta cimma matsaya guda tsakaninsu don daddale wasu yarjejeniyoyi da aiwatar da su a tsanake.

Bayan taron, wakilin kasar Iran a hukumar IAEA ya fada wa manema labaru cewa, cikin shekaru 10 da suka gabata, hukumar IAEA ba ta gano wata shaidar dake nuna cewa, Iran na habakar makaman nukiliya, kuma Iran tana fatan yin shawarwari game da fasahohi da hukumar IAEA, amma bai kamata hukumar IAEA ta sanya siyasa ba a yayin da take gudanar da aikinta.(Bako)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China