in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An kammala aikin yin rajistar 'yan takarar shugabancin kasar Iran
2013-05-12 16:35:03 cri
Bisa alkaluman da ma'aikatar harkokin cikin gida ta kasar Iran ta gabatar a daren ranar Asabar 11 ga wata, ya zuwa yammacin wannan rana, an riga an kammala aikin yin rajistar 'yan takarar shugabancin kasar, inda adadin ya nuna cewa, baki daya mutane 686 ne suka nuna sha'awar shiga wannan takara.

Ranar 11 ga watan dai itace rana ta karshe ga aikin na rajista, kuma kafin kammala wannan aiki, babban wakilin kwamitin shawarwari kan batun nukiliya na Iran, kana sakataren kwamitin koli na tsaron kasar, Saeed Jalili, da tsohon ministan harkokin waje na kasar, Ali-Akbar Velayati, da tsohon shugaban kasar, Akbar Hashemi Rafsanjani, da babban mai ba da shawara ga shugaban kasar Iran, Esfandiyar Rahim-Mashaei dukkansu sun ziyarci ma'aikatar harkokin cikin gida domin yin rajistan shiga takarar.

Bisa labarin da aka bayar, an ce, bayan kammala wannan aiki, kwamitin sa ido kan kundin tsarin mulkin kasar ta Iran, zai fara yin bincike kan 'yan takarar, kuma zai gabatar da takardar sunayen 'yan takara ta karshe nan da makwanni biyu masu zuwa.

Za a gudanar da babban zaben kasar Iran ne dai a watan Yuni dake tafe.(Fatima)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China