in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban Sin Xi Jinping ya gana da shugabannin kasar Trinidad and Tobago da kuma firaministan kasar Antigua and Barbuda
2013-06-02 16:50:54 cri

A ranar 1 ga watan na Yuni a Puerto Espana, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya gana da takwaransa na kasar Trinidad and Tobago Anthony Carmona.

Xi ya bayyana cewa, kasar Trinidad and Tobago kasar farko ce da ya kai ziyara a yankin Caribbean bayan da ya hau kujerar shugaban kasar Sin, kana ita ce zango na farko a ziyararsa a yankin Latin Amurka da Caribbean. Yayin wannan ziyara, ana sa ran kara hadin gwiwa a tsakanin kasashen biyu, da kuma inganta dangantakarsu zuwa wani sabon matsayi.

Shugaba Carmona ya bayyana cewa, kasarsa tana son kara yin mu'amala tare da kasar Sin da yin hadin gwiwa a tsakaninsu musamman a fannonin tattalin arziki, cinikayya, makamashi masu tsabta, kiyaye muhalli da dai sauransu. Kana kasarsa na fatan kara yin mu'amalar al'adu a tsakaninta da kasar Sin, da kuma kara fahimtar juna da zurfafa zumunci.

1 2 3
Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China