Bisa goron gayyata da shugaban jamhuriyar Trinidad and Tobago Anthony Carmona, da shugaban kasar Costa Rica Laura Chinchilla, da shugabar kasar Mexico Enrique Peña Nieto, da shugaban Amurka Barack Obama suka gabatar, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya bar birnin Beijing a ranar 31 ga wata da safe, don ziyarar aiki a kasashen Trinidad and Tobago, da Costa Rica, da Mexico, kuma zai halarci shawarwarin da za a yi tsakanin shugabannin kasashen Sin da Amurka.(Bako)