in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban kasar Sin ya ce ziyarar sa a Trinidad da Tobago,domin kara karfi ne a dangantakar kasashen biyu
2013-06-01 16:11:27 cri
Shugaban kasar Sin Xi Jinping yace ziyarar aikin da ya kai kasar Trinidad da Tobago zai kara karfi wajen inganta dangantakar dake tsakanin kasashen biyu.

A sanarwar da aka fitar da saukar sa birnin port na spaniya,Shugaba Xi ya ce za'a karfafa hulda da kara ciyar da hadin gwiwwa gaba tsakanin Sin da Trinidad da Tobago wanda hakan ba ma kawai zai amfana ma al'ummomin kasashen biyu ba har ma zai kara hada kai da inganta zumunci tsakanin kasar ta Sin da sauran kasashe na yankin Caribbean dama sauran kasashen dake tasowa.

Shugaban na kasar Sin ya samu tarba daga wajen takwaransa na Trinidad da Tobago Anthony Carmona,da Firaministan kasar Kamla Persad-Bissessar da sauran shugabannin kasar,inda shuagaba Carmona ya shiya wani liyafar maraba ma Shugaban kasar na Sin.

Shugaba Xi wanda shi ne Shugaban kasar Sin na farko da ya ziyarci kasar Trinidad da Tobago tun lokacin da kasashen biyu suka kulla huldar diplomasiyya a shekara ta 1974, ana kuma sa ran zai tattauna da shugaba Carmona da kuma firaminista Persad-Bissessar game da yadda za'a inganta dangantakar hadin gwiwa tsakanin kasashen 2.(Fatimah Jibril)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China