in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kungiyar tarayyar kasashen Afrika AU ta yi alawadai da hari a Nijar
2013-05-24 09:52:32 cri

A jiya alhamis 23 ga wata kungiyar tarayyar kasashen Afrika AU ta yi alawadai da harin kunar bakin wake da aka kai a garuruwan Arlit da Agadez na jamhuriyar Nijar.

Cikin wata sanarwa, shugabar kungiyar Nkosazana Dlamini-Zuma ta yi suka da babbar murya kan wadannan hare-hare har guda biyu da suka auku a safiyar jiyan, tana mai nuna cikakken goyon bayanta ga gwamnatin kasar Nijar a kokarinta na yaki da ta'addanci.

Haka kuma madam Zuma ta jaddada godiyarta ga kasar ta Nijar bisa ga gudunmuwar sojin da ta bayar domin taimaka ma wata kasar a nahiyar wato Mali yakan ta'addanci.

Shugabar kungiyar ta AU ta ce, tsagerancin 'yan ta'adda a Nijar ya nuna bukatar dake akwai ga daukacin kasashen Afrika da su hada kai su yake wannan batu tare da sauran miyagun ayyuka da suka ratsa cikin nahiyar.(Fatimah)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China