in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin ta jaddada cewar za ta nace ga bin manufar yaki da ta'addanci
2011-08-04 20:45:17 cri

A ran 4 ga wata, ministan tsaron zaman lafiyar jama'a na kasar Sin Meng Jianzhu ya bukaci hukumomi daban daban na yankuna kasar Sin da su yi nazari kan halin yaki da ta'addanci, da aiwatar da manufofin yaki da ta'addanci, da nacewa ga bin manufar yaki da ta'addanci, da kiyaye zaman lafiya da dukiyar jama'ar kasar.

A kwanan baya, an kai hare-hare a jere a jihar Xinjiang ta kasar Sin, wadanda suka yi sanadiyar mutuwar mutane da yawa, da kuma kawo barazana ga bunkasa tattalin arzikin jihar da hadin kan kabilun jihar. Gwamnatin kasar Sin tana mai da hankali sosai ga hare-haren, kuma shugabannin kasar Sin sun ba da umurni ga hukumomin da abin ya shafa da su yi nazari kan hare-haren da kuma ayyukan yaki da ta'addanci.

A gun taro kan yaki da ta'addanci da aka shirya a ran 4 ga wata, Meng Jianzhu ya bukaci hukumomi daban daban da abin ya shafa da su aiwatar da matakan yaki da ta'addanci, da yin kokari wajen kiyaye zaman lafiya a jihar.(Abubakar)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China