in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Babban jami'in jihar Xinjiang mai cin gashin kanta ta kasar Sin ya yi furucin cewa za'a dauki kwararen matakan da suka dace domin yaki da masu tsatsauyin ra'ayin addini
2011-08-08 14:49:43 cri

Zhang Chunxian, babban sakataren kwamitin jam'iyyar kwaminis ta kasar Sin na yankin jihar Ouigoure ta Xinjiang mai cin gashin kanta dake arewa masu yammacin kasar ya ba da umurnin gudanar da kamfen yaki da masu tsatsauyin ra'ayin addini dake hannu kan tashe tashen hankalin baya bayan nan.

Mista Zhang Chunxian ya yi wadannan kalamai a lokacin wani taron da gwamnatin yankin ta kira bayan wasu jerin hare hare ukku da aka kaiwa jihar ta Xinjiang.

Baya da haka mista Zhang ya mika kiransa ga kwararru da ma'aikata da su ba da taimako sosai domin yaki ba tare da kasala ba kan wasu ayyukan addini dake adawa da dokar kasa da kuma ake amfani da addini domin rura wutar gaba tsakanin kabilun kasar da kuma hada kai wajen kai hare haren ta'addanci, in ji kafofin watsa labarai na jihar a ranar yau Litinin. ( Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China