in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An gano mutane 129 da suka kamu da cutar murar tsuntsaye mai nau'in H7N9 a kasar Sin
2013-05-07 16:20:04 cri
Bisa labarin da hukumar kula da kiwon lafiya da tsara shirin haihuwa ta kasar Sin ta bayar, an ce, daga ranar 1 ga watan Mayu da karfe 4 na yamma zuwa ranar 6 ga wata da karfe 4 na yamma, an kara samun mutane biyu da suka kamu da cutar murar tsuntsaye mai nau'in H7N9, kuma dukkansu sun fito daga lardin Fujian na kasar Sin.

Ya zuwa yanzu, an tabbatar da mutane 129 da suka kamu da cutar murar tsuntsaye, cikinsu mutane 31 sun mutu, kuma mutane 42 sun wartsake.

A ranar 6 ga wata, hukumar kula da kiwon lafiya da tsara shirin haihuwa ta bayar da labari a shafinta na Internet cewa, kwanan baya, mujallar kimiyya ta Birtaniya "Nature" ta yi bayani cewa, gwamnatin Sin ta dauki kwararan matakai cikin hanzari don yaki da cutar murar tsuntsaye, don haka wajibi ne a jinjina kokarin gwamnatin Sin wajen bayar da rahoto da labaru a bayyane.(Bako)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China