in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasashen duniya sun yaba wa kokarin da kasar Sin ta yi wajen ceton mutanen da bala'in girgizar kasa na Lushan ya ritsa da su
2013-04-23 16:34:45 cri
Game da halin da ake ciki na girgizar kasa mai maki 7 da ta fada wa gundumar Lushan da ke lardin Sichuan a kasar Sin a ranar 20 ga wata, kasashen duniya sun ci gaba da mai da hankali game da lamarin, sannan wasu kafofin yada labaru su ma sun yaba wa kokarin da gwamnatin da jama'ar kasar suka yi wajen ceton mutane.

Shafin Internet na Afrika ta Kudu ya ba da labari cewa, bayan aukuwar girgizar kasa, kungiyar ceton mutane ta kasar Sin ta je yankunan da bala'in ya ritsa da su ba tare da bata lokaci ba don ceton mutane. Bisa labarin da aka bayar, an ce, sabo da wahalar tafiya zuwa wurin, an gamu da cikas wajen ceton mutane, sabili da haka, jama'a da dama suna bukatar ruwan sha da tantuna a wuraren da bala'in ya shafa.

Su ma, jama'ar kasar Nijeriya sun nuna damuwa sosai game da bala'in girgizar kasa, inda suka aika da wasikun jaje ga wakilin gidan rediyon CRI da ke Nijeriya, don nuna tausayi ga jama'ar kasar Sin. Daya daga cikinsu Hajiya Suwaiba Suleiman dake aiki a gidan rediyon Aso dake birnin Abuja hedkwatar tarayar Nijeriya wadda ke da wasu labaru na kasar Sin sosai. Ta sanar da wakilinmu cewa, abin da ya burge ta game da kokarin ba da ceton shi ne, yadda bayan aukuwar girgizar kasa, firaministan kasar Sin Li Keqiang ya je yankunan da girgizar kasa ta shafa da kanshi ba tare da bata lokaci ba. Ta ce, da isar Mr. Li wannan wuri ya sa hannu wajen aikin ceto. Ganinta, wannan ya nuna cewa, shugabannin kasar Sin sun san yadda za su yi a ayyukansu don moriyar jama'a da dukuyoyin mutane ba tare da ba da kaskanci ga jama'arsu ba, wannan abin koyi ne sosai.(Bako)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China