in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban kasar Masar ya nuna fatan shiga kungiyar kasashen BRICS
2013-03-21 15:08:28 cri
Bayan ziyarar aiki a kasar Pakistan, shugaban kasar Masar Mohamed Morsy, ya ci gaba da ziyarar aiki ta kwanaki uku a kasar India tare da tawagar da ke karkashin jagorancinsa.

Yayin wannan ziyarar, shugaba Morsy ya nuna cewa, kasar Masar na fatan shiga kungiyar kasashen BRICS, don farfado da tattalin arzikinta.

Yayin taron dandalin tattaunawar harkokin cinikayya tsakanin kasar India da kasar ta Masar da aka yi ran 20 ga wata, shugaba Morsy ya bayyana cewa, a shirin gaggauta farfadowar tattalin arzikin kasar ta Masar, kasarsa na fatan shiga kungiyar kasashen BRICS, ta yadda za ta karfafa hadin gwiwa tsakaninta da kasar India, da dai sauran kasashen dake bunkasa cikin sauri a fannin na tattalin arziki. Har ma ya ambata wani sabon suna da ya kira E-BRICS, wato Egypt da BRICS ke nan, idan har kasar tasa ta samu damar shiga cikin kungiyar.

Morsy ya kuma nuna cewa, bisa gayyatar da aka yi masa, zai halarci taron kolin kasashen BRICS da za a kira a kasar Afirka ta Kudu, a karshen watan Maris. Yana fatan za a ciyar da shirin kafa bankin zuba jari tsakanin kasashe masu tasowa, don ba da taimako ga kasashen wajen inganta ababen more rayuwa ga al'ummunsu cikin sauri. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China