in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kafofin yada labaru na kasashen duniya sun dora muhimmanci sosai game da ziyarar sakataren harkokin wajen Amurka a kasar Sin
2013-04-15 15:10:44 cri
A ranar 13 ga wata, sakataren harkokin wajen kasar Amurka John Forbes Kerry da ya kawo ziyarar aiki a kasar Sin, da daidai ne ya gana da shugaban kasar Sin Xi Jinping da firaministan kasar Li Keqiang da sauran shugabannin kasar Sin. Kwararru da kafofin yada labaru na wasu kasashen duniya sun dora muhimmanci sosai game da ziyarar farko ta Kerry a kasar Sin, bayan da ya zama sakataren harkokin wajen Amurka.

Jaridar Washellongton Post ta bayar da labari a shafinta na Internet cewa, kasar Sin ta yi kira da a yi shawarwari don warware halin kunci a zirin Koriya cikin ruwan sanyi, kana kuma jaridar New York Times ta ba da labari cewa, Kerry ya ce, idan Koriya ta Arewa ta yi watsi da shirin makaman nukiliya, kila ne, Amurka za ta rage tsarin kakkabo makamai masu linzami.

Ban da wannan kuma, kamfanin dillancin labaru na AFP da na kasashen Japan da Koriya ta Kudu sun bayyana cewa, kasashen Sin da Amurka sun amince da kawar da makaman nukiliya a zirin Koriya cikin lumana.

A yayin ziyarar Kerry a kasar Sin, kasashen Sin da Amurka sun tattauna batun sauyin yanayi, da tsaron yanar gizo ta Internet. Bugu da kari kuma, a cikin bayanin da kamfanin dillancin labaru na Reuters da na AFP suka bayar, an ce, kasashen Sin da Amurka sun bayyana cewa, ya zama dole a inganta tsaron yanar gizo ta Internet da batun sauyin yanayi a duniya, don haka za a kafa wani rukunin daidaita batun tsaron yanar gizo da wani na daban don tabbatar da batun sauyin yanayi na duniya.(Bako)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China