in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sakataren harkokin wajen kasr Amurka John Kerry ya fara ziyara a kasar Sin
2013-04-13 16:00:22 cri
Bisa gayyatar da Wang Yi, ministan harkokin wajen kasar Sin ya yi masa ne, Mr. John Kerry, sakataren harkokin wajen kasar Amurka ya isa nan Beijing yau 13 ga wata da safe, kuma ya fara ziyara a kasar Sin.

Wannan ne karo na farko da John Kerry ya kawo wa kasar Sin ziyara bayan da ya hau kan mukaminsa. Wannan ne kuma wani muhimmin jigo na daban da ya kawo wa kasar Sin ziyara domin ganawa da muhimman jigunan kasar Sin bayan da Jacob Lew, wakilin musamman na shugaba, kuma ministan kudi na gwamnatin kasar Amurka ya kawo ziyara kasar Sin a watan Maris bayan da aka rantsar da sabbin gwamnatocin kasashen Sin da Amurka.

Bisa labarin da ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin ta bayar, an ce, a yayin ziyararsa a nan kasar Sin, shugabannin kasar Sin za su gana da shi, inda za su yi musayar ra'ayoyi kan huldar dake tsakanin kasashen Sin da Amurka da sauran batutuwan da suke jawo hankulansu tare.

Wannan ne kuma zango na biyu cikin ziyararsa ta kasashen gabashin Asiya guda uku. Kafin ya zo kasar Sin, ya riga ya kai ziyara a kasar Koriya ta kudu, sannan zai kai ziyara ga kasar Japan gobe ranar 14 ga wata. (Sanusi Chen)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China