WHO ta jinjinawa fara gudanar da rigakafin COVID-19 a kasashen Afirka
2021-03-12 09:52:52 CRI
Daraktan shiyyar Afirka a hukumar lafiya ta duniya WHO Mr. Matshidiso Moeti, ya ce aikin rigakafin COVID-19 na gudana yadda ya kamata a sassan nahiyar Afirka, duba da yadda tuni adadin wadanda suka karbi rigakafin cutar ya kusa miliyan 4.
Matshidiso Moeti, wanda ya yi wannan tsokaci a jiya Alhamis, cikin wata sanarwa da aka fitar a birnin Nairobin kasar Kenya, ya ce isar karin alluran rigakafi nahiyar, zai karfafa tasirin dakile yaduwar wannan annoba.
Sai dai kuma a cewar jami’in, a yanzu, ma’aikatan lafiya dake kan gaba wajen tunkarar cutar, da sauran mutane masu yanayi na musamman ne ake baiwa muhimmanci, wajen karbar rigakafin cutar ta COVID-19. Nairobi.
A cewar hukumar WHO, kasashen nahiyar Afirka 22, sun riga sun karbi sama da alluran rigakafin COVID-19 miliyan 14.6, tun daga ranar 24 ga watan Febrairun da ya gabata, karkashin shirin nan na COVAX. (Saminu)
Labarai Masu Nasaba
- Kasashen Afirka na ci gaba da karbar alluran riga kafi daga shirin COVAX
- Habasha ta karbi kashin farko na rigakafin COVID-19 miliyan 2.2 daga shirin COVAX
- Najeriya ta karbi riga-kafin COVID-19 miliyan 3.94 da ta jima tana tsammaninsa
- WHO:Kasashen Afirka sun fara cin gajiyar alluran riga kafi karkashin shirin COVAX