logo

HAUSA

Najeriya na daukar matakan hana yaduwar cutar COVID-19

2020-03-25 09:21:10 CRI

Najeriya na daukar matakan hana yaduwar cutar COVID-19


A yayin da cutar numfashi ta COVID-19 ke ci gaba da bazuwa a duk fadin duniya, kasashen Afirka daban-daban na fuskantar babbar barazanar yaduwar cutar, ciki har da tarayyar Najeriya, kasa da ta fi yawan al'umma a duk fadin nahiyar Afirka.

Najeriya na daukar matakan hana yaduwar cutar COVID-19

To, menene ya kamata mutanen Najeriya su fahimta game da cutar? Yaya za'a yi domin kare kai daga kamuwa da cutar? Ko akwai darussan da Najeriya da ma sauran kasashen Afirka za su iya koya daga kasar Sin, sakamakon dimbin nasarorin da ta cimma wajen ganin bayan annobar cutar?

Najeriya na daukar matakan hana yaduwar cutar COVID-19

Game da wadannan batutuwa, wakilinmu Murtala Zhang ya zanta da wasu masana a bangaren lafiya na Najeriya, domin su tofa albarkacin bakinsu kan matakan da gwamnatin Najeriya ta dauka wajen hana yaduwar cutar COVID-19, da ra'ayinsu kan kokarin da gwamnatin kasar Sin ta yi a wannan fanni.

Najeriya na daukar matakan hana yaduwar cutar COVID-19

Wadannan masanan su ne, Dr. Nasiru Sani Gwarzo, kwararren likita a bangaren yaki da cututtuka na al'umma, kana likita mai yaki da cututtuka masu yaduwa a Najeriya, da Dr. Imam Wada Bello, babban darakta mai kula da lafiyar al'umma da cututtuka ta ma'aikatar lafiya dake jihar Kano a Najeriya.(Murtala Zhang)