in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Masanan kasa da kasa sun zargin Amurka cewar, ta lalata tsarin ciniki tsakanin kasa da kasa
2018-04-12 11:10:02 cri
Kwanan baya, wasu masanan kasa da kasa sun yi nazari kan takarddamar ciniki da Amurka ta tayar a tsakaninta da kasar Sin, inda suka bayyana cewa, dukkanin matakan da kasar Amurka ta dauka sun nuna rashin tabbaci na kanta, wadanda suka kuma bata tsarin ciniki a tsakanin kasa da kasa. Haka kuma, za a iya warware takarddamar ne ta hanyar yin shawarwari kawai.

Tsohon mashawarcin jakada kan harkokin tattalin arziki na Afirka ta Kudu dake kasar Sin Yusuf Adam ya bayyana cewa, mai yiyuwa ne matakan da kasar Amurka ta dauka za su haddasa barazana ga yanayin tattalin arzikin duniya, bai kamata kasashen duniya su yi shiru kan wannan batu ba, sai a dauki matakan tinkarar matsalar cikin sauri.

Wani malamin jami'ar Kenyatta ta kasar Kenya ya bayyana cewa, kasar Sin tana aiwatar da harkokinta yadda ya kamata ta fuskar babban kuskuren da kasar Amurka ta yi. Kuma Sin ta nuna aniyarta ta kiyaye tsarin cinikin duniya, lamarin da ya sa kaimi ga kasa da kasa wajen yin adawa da matakin kariyar cinikin da kasar Amurka ta yi, da kuma bada tabbaci ga kasa da kasa wajen karfafa dunkulewar kasa da kasa a fannin tattalin arziki. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China