A watan Maris na shekarar 2011, an barkar da rikicin Syria. A cikin shekarun 12 da suka gabata, kasar Amurka na ci gaba da kai dauki daga dakarun soji da saka haramtattun takunkumi ta gaban kai ga Syria, lamarin da ya haddasa bala'o'in jin kai masu yawa. An tilastawa jama’ar kasar da dama tserewa daga gidajensu, kuma iyalin Hussein el Jadoua’a sun yi tattaki zuwa kasar Lebanon dake makwabtaka.
Malam Abbas Ibrahim, dalibi ne dake karatun digiri na uku a halin yanzu a kasar Indiya, kuma ma’aikaci ne a jami’ar jihar Bauchi dake tarayyar Najeriya. Duk da cewa malam Abbas Ibrahim bai taba zuwa kasar Sin ba, amma ya dade yana sauraren shirye-shiryen sashin Hausa na gidan rediyon kasar wato CRI, kuma ya san abubuwa da yawa game da kasar. A zantawar sa da Murtala Zhang, malam Abbas Ibrahim ya yi tsokaci kan ci gaban da kasar Sin ta samu......
A wannan makon ne, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya kai ziyarar aiki kasar Rasha daga ranar 20 zuwa 22 ga watan Maris. Wannan ita ce ziyara ta farko da Xi Jinping ya kai zuwa ketare, tun bayan da aka sake zabarsa a matsayin shugaban kasar, kuma ziyara ce ta sada zumunci da tabbatar da hadin gwiwa da zaman lafiya, da karfafa dangantakar hadin gwiwa bisa manyan tsare-tsare tsakanin Sin da Rasha a sabon zamani.
A kwanan baya, shugaban kasar Nijar, Mohamed Bazoum ya jagoranci wani zaman taro na manyan jami ai kan zuba a fannin wasannin motsa jiki musammun ma game da wasan kwallon kafa a fadar shugaban kasa dake birnin Yamai, ganin yadda kasar Nijar take kokarin kama hanya a bangaren wasan tama’ula da ma sauran wasannin motsa jiki a dandalin kasa da kasa.
A yayin babban taron tattaunawa tsakanin Jam'iyyar Kwaminis ta kasar Sin da jam'iyyun siyasa na duniya da aka gudanar ta kafar internet a kwanakin baya, shugaban kasar Sin Xi jinping ya gabatar da shawarar wayewar kai ta duniya. A cikin shirinmu na yau za mu saurari ra'ayin wani shahararren shehun malami dan kasar Mali dangane da wannan shawara, gami da rawar da jam'iyyar Kwaminis ta kasar Sin ke takawa a duniya.