01-Apr-2025
31-Mar-2025
27-Mar-2025
26-Mar-2025
20250401-Yamai
00:00
1x
Duk da cewa tattalin arzikin duniya na cikin wani yanayi na wargajewa da karuwar rashin tabbas, kasar Sin ta sake jaddada aniyar samun ci gaba mai inganci da hadin gwiwa tare da sauran kasashen duniya don cimma nasar tare, da shawo kan kalubalen da duniya ke fuskanta ta hanyar gabatar da sabbin dabarun gudanar da ayyuka da sabbin fasahohi musamman na zamani. A taron dandalin raya kasa na kasar Sin na shekarar 2025 da aka kammala a makon da ya gabata.
A matsayinsa na zama sahun gaba wajen zurfafa hadin gwiwar tattalin arziki da cinikayya tsakanin Sin da Afirka, lardin Hunan na daya daga cikin lardunan da ke tsakiyar kasar Sin wajen yin hadin gwiwa a fannin tattalin arziki da cinikayya da kasashen Afirka. Kididdigar hukumar kwastam ta birnin Changsha dake lardin Hunan ta nuna cewa, yawan cinikin da lardin Hunan ya yi da kasashen Afirka a bara ya kai Yuan biliyan 54.85, inda ya ci gaba da zama na farko a yankunan tsakiya da yammacin kasar. A cikin shirinmu na yau, bari in gabatar muku da wasu nasarorin da aka samu a fannin hadin-gwiwar tattalin arziki da cinikayya tsakanin lardin Hunan da kasashen Afirka.
02-Apr-2025
17-Mar-2025
30-Mar-2025
29-Mar-2025
28-Mar-2025
Saboda sha’awar su ga kasar Sin, suka zo kasar, saboda mafarkinsu na nan gaba, suka zauna a kasar. Lokacin da baki suka yi “ido biyu kasar Sin”, wane shauki ne ke tasowa a zukatansu daga a daidai wannan lokaci? Mun tsara jerin shirye-shirye masu suna “Haduwa da Sin”, don sauraron labaran da suka faru a tsakanin wasu yan kasashen waje da kasar Sin. Inkara yar kasar Kazakhstan ce dake da suna ta Sinanci Zhou Mingying. Mingying, ta zo kasar Sin ne tare da mahaifiyarta tun tana karama, ta ce birnin Fuzhou na kasar dake da yanayi mai kyau, ya kyautatawa lokacin kuruciyarta, kuma birnin Beijing, mai karbar dukkan al’adu, ya bude mata hanyar cika mafarkinta.