Ni hao
Ina fata kuna lafiya kamar yadda muke a nan birnin Abuja, Najeriya.Allah Ya taimaka.
Mun ga sabuwar gasar kacici-kacici da kuka wallafa a shafinku. Gaskiya abin yayi kyau sosai, musamman ma yanzu da mutane masu yawan gaske ke dada tururuwa zuwa kasar Sin domin samun harkokin ci gaba da kuma alheri. Sannan kuma gasar yayi kyau saboda ya dace da bikin cikon shekaru 75 da kafuwar CRI. Ina taya ku murna, da fatan Allah Yasa ku kara bunkasa sosai.
Sai naji daga gareku.
Salisu Muhammad Dawanau
Abuja, Najeriya