Ina fata kuna lafiya. Allah Ya taimaka.
A yau, kusan duk kafofin yada labaran Najeriya suna da masaniyar wannan ziyara ta Shugaba Muhammad Buhari zuwa kasar Sin a ranakun 11 zuwa 15 ga Afirilu, kuma kowa na sane da kyakkyawar alaka dake tsakanin Sin da Najeriya.
A gaskiya, wannan ziyara ta zo a daidai lokacin da ta dace musamman domin yanzu ne ake so a kammala yarjejeniya a kan aikin jirgin kasa na Najeriya, sannan da wasu batutuwa masu muhimmanci na kara karfafa dankon zumunci dake tsakanin juna.
Muna fata za a yi nasara, sannan kuma kasashen namu zamu amfana da wannan ziyara. Muna kuma fata Shugaba Xi Jinping nan gaba shi ma zai kawo ziyara nan Najeriya.
Allah Ya taimaka.
Salisu Muhammad Dawanau