Zuwa ga malama Fatima Liu, sashin hulda da masu sauraro cri Hausa. A ranar talata 10 ga watan 06 shekara ta 2014, na karanta wani saban nazari da malama Tasallah ta gabatar mana adangane da yadda yaka mata iyaye su kiyaye lafiyar yaransu dan kare lafiyar yaransu daga harbuwa da cutuka da kan addabi yara, kamar cutukan tari da dai sauransu. Hakika, idan iyayen yara suka maida hankali ga wannan saban nazari da malama Tasallah ta kawo mana a filinta na kiwon lafiya, na yi amanna cewa, za su samu ilmin kula da lafiyar yaransu yadda yaka mata ainun. Daga karshe, ina mai yaba wa malama Tasallah da cri Hausa, bisa kokarinsu na kawo mana tsarabar masamman a wannan shiri na kula da lafiyar mutane.
Daga Alhaji Ali kiraji Gashua.