in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Tawagar COMESA ta isa Malawi don sanya ido a zaben kasar
2019-05-16 09:46:01 cri
Tawagar wakilan yan kasuwa na kasashen gabashi da kudancin Afrika (COMESA), ta isa kasar Malawi, don sanya ido a zabukan kasar uku da za'a gudanar a ranar 21 ga watan Mayu, kwanaki shida gabanin ranar jefa kuri'ar.

Wata sanarwar da shugaban gudanarwar kungiyar ta COMESA, Elizabeth Mutunga, ta bayyana cewa, ambassada Mohamed Ahmed Abdelghaffar Karrar shi ne zai jagoranci tawagar, jami'in wanda shi ne shugaban kwamitin dattawa na kungiyar COMESA wanda ya fito daga jamhuriyar Sudan.

Sanarwar ta ce shugaban tawagar wakilan zai isa kasar ne a ranar 17 ga watan Mayu, kwanaki hudu kafin gudanar da zaben.

A cewar sanarwar, masu sa ido na COMESA za su duba irin shirye shiryen da aka yi gabanin fara zaben wanda ya kunshi tuntubar jam'iyyun siyasar kasar, da hukumar zaben kasar ta Malawi (MEC), da jami'an tsaron kasar, da kungiyoyin fararen hula, da kafafen yada labarai, da kuma sauran masu ruwa da tsaki a harkokin zaben kasar. (Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China